Wani babban jami’in hukumar agajin gaggawa na MDD, yace an tada bam kan wani ayarin motocin hadin guiwan MDD da kungiyar Red Crescent ta Syria a jiya Litini a birnin Aleppo dake yammacin Syria, da ya kashe ma’aikatan kai kayan agaji da dama, wadansu kuma suka jikata.