Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kungiyar IS Ta Harba Wata Roka Sansanin Sojan Sama Na Qayyarah


Wani hafsin sojin Amurka yace ana tuhumar cewa mayakan kungiyar IS ne suka harba rokan da ya sauka a sansanin soja dake Arewacin Iraqi wanda kuma watakila yake dauke da gubar iskar gas ta Mustard – watau Riɗi.

A zantawarshi da manema labarai a ma’aiakatar tsaron Amurka ta Pentagon jami’in da ba a bayyana sunasa ba yace babu wanda ya samu rauni a wannan harin da aka kai sansanin sojan sama na Qayyarah amma daruruwar sojojin Amurka na jibge a wurin a lokacin harin.

Jami'in yace rokan ya fado a cikin harabar da jami’an tsaron suke amma ya kira wannan hari a matsayin mara muhimmanci ga aikin soji kuma bai da wani tasiri a kan ayyuka da sojojin ke gudanarwa ta kowace hanya.

Sansanin sojojin na Yammacin Qayyarar wuri da aka kebewa sojojin Iraqi don shirya hare hare akan garin Mosul, birnin da tun shekaru biyu da suka wuce yake zaman mazaunin mayakan kungiyar IS.

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 3:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 2:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG