Kungiyar kare hakkin bil adama ta Amnesty International, ta fitar da rahotonta na shekara-shekara, kan yadda ake taka hakkin bil adama a kusan kasashen 160, tana mai ikrarin cewa shekarar 2017, ita ce shekarar da aka fi ganin nuna kiyayya irin ta siyasa, da kuma yadda wasu shugabannin duniya suka jefa fargaba a zukatan mutane.