Wa'adin da wata kungiyar matasa ta bai wa gwamnan jihar Abia, Okezie Ikpeazu, na ya tsige mahaifin Nnamdi Kanu, Israel Okwu Kanu daga sarautarsa, ya cika, inda suka zarge shi da kin ja wa dansa kunne kan fafutukar da yake yi wacce suka ce ta kassara harkokin yau da kullum a yankin.