Mai bincike na musamman Robert Mueller ya yi bincike game da lokuta 11 wanda ya ke kyautata zato cewa Shugaba Donald Trump ya karya doka a kokarin dakatar da bincikensa.
Firayim Ministan kasar Mali Soumeylou Boubeye Maiga da dukan mambobin gwamnatinsa sun yi murabus a jiya Alhamis.
A yau Laraba ne ‘yan kasar Indonesia suka fara kada kuri’a wanda ya zama zabe mafi girma da za’a gudanar a cikin rana guda.
‘Yar Shugaban kasar Amurka Donald Trump kuma mai ba da shawarwari a fadar White House, Ivanka, ta ziyarci kasar Ivory Coast a ziyarar aiki ta kwanaki hudu da take yi domin inganta tattalin arzikin mata a yankin yammacin Afrika.
Rahotanni a baya-bayan nan na cewa, kudin dake asusun ajiya na kasar China zai kare a shekara ta 2035, wannan ya janyo cece kuce a hanyar sadarwa ta Internet.
Masu zanga-zanga a Khartoum suna ci gaba da neman shugaban kasar Omar al-Bashir da yayi murabus, a cigaba da zaman da suke yi a hedkwatar sojan kasar, inda aka ji karar harbin bindiga.
Akwai alamun dake nuna cewa mai yiyuwa ne Firma Ministan Israili Benjamin Netanyahu zai yi nasarar samun wa’adi na 5 na mulki bayan da sakamakon zabe ya nuna cewa jami’yyar sa ta Likud ne zata iya lashe zaben.
Sababbin dokokin da masarautar Brunei ta fito da su a kan hana zina da luwadi a kasar sun janyo wa kasar kulawar sauran kasashe dake nuna jin haushin daukar wadanan matakan.
An fara gagarumin aikin alluran rigakafin cutar kwalara a kasar Mozambique don hana yaduwar cutar daga juyawa zuwa annoba mai tsanani.
An kama wata mace ‘yar kasar China bayanda ta kutsa cikin jerin gidajen hutawa na shugaban Amurka Donald Trump dake jihar Florida, inda kuma aka same ta dauke da wata na’urar komputa mai lahani a cikinta.
Dubban dubatan fararen hula da suka gudu daga garin Malakal na Sudan ta Kudu lokacin yakin da ya barke a shekarar 2013 sun koma gidajensu.
Jami'ai a kudancin Afganistan sun ce akalla mutane hudu sun mutu kuma fiye da 30 sun jikkata a fashewar wasu tagwayen boma bomai, a wajen wani bikin baje kayan noma da akeyi duk sabuwar shekara.
Bincike na musamman na Robert Mueller ya kamala.
Hukumar tara kudaden shiga ta kasar Sudan ta Kudu tana barazanar fallasa jami'an gwamnati da na bankuna da suka saci kudaden shiga.
'Yan bindiga sun kai hari a yau Laraba a wani sansanin tsaro a kudu maso yammacin Pakistan, inda suka kashe akalla dakarun soji shida.
A yau Laraba ake sa ran yankewa tsohon shugaban yakin neman zaben shugaban Amurka Paul Manafort hukuci , a kotun tarayya dake nan Gundumar Kwalambiya, akan laifufuka guda biyu.
Gwamnatin shugaban Amurka Donald Trump na dari-dari dangane da kiran da ake yi a cikin gida da kuma kasashen duniya, akan ta dakatar da amfani da jiragen sama, wanda a cikin watanni 6 ya kashe sama da mutane 350.
Domin Kari