A yau Laraba ake sa ran majalisar dokokin kasar Birtania zata kada kuri’a kan ko ya Birtaniya za ta fice daga kungiyar kasashen turai, batare da amincewa da wasu ka’idojin ficewar ba.
Wasu da ba'a san ko su wanene ba sun Harbe dan takarar Sanata a tutar jam'iyar ADP, Hon. Temitope Olatoye (Sugar) a Jihar Oyo.
Matsalar na'urarar tantance masu kada kuri'a da kuma saye ko saida kuri'a na daga cikin batutuwan da masu sa ido na cikin gida suka koka akai dangane da zaben gwamnoni da akai jiya a Najeriya.
Wasu 'yan kunar bakin wake da ake zargin 'yan kungiyar Boko Haram ne yi kokarin kai hari a wani Cocin Katolika dake burnin Shawu, dake jihar Adamawa.
A jihar Sakkwato an sami fitowar jama'a sosai a runfunan zabe, sabanin jahohin Zamfara da Kebbi.
Mata da masu fama da lalurar nakasa na daga cikin dubban mutanen da sukayi tururuwa zuwa rumfunan zabe domin kada kuri'ar su a zaben Gwamna da 'yan Majalisar Dokokin Jihar Neja a Najeriya.
A jihar Katsina kayan aiki da ma’aikatan zabe tare da wakilan jam’iyyu wato “Agent” da kuma jami’an tsaro duk sun isa tashoshin zabe da wuri.
rahotannin dake fitowa daga birnin Legas na nuna cewa mutane da dama basu fito ba domin zabe, duk da yake an gudanar da zaben cikin kwanciyar hankali da lumana a birnin.
An samu karancin fitowar masu zabe a wasu sassan jihohin Adamawa da Taraba, a zaben gwamnoni da na 'yan majalisar dokokin jihohi da ake yi yau Asabar, a Najeriya.
Manyan ‘yan takara na jam’iyyu APC da PDP da sauran jam’iyyu fiye da 50 na fafatawa a neman kujerar gwamnan Kano, sai dai 'yan sanda sun kama wata mota makare da takardu da ake zargin kuri'un zabe ne.
Rahotanni daga jihohin Bauchi da Gombe na cewar zaben gwamna da na 'yan majalisun dokoki a jihohin biyu, yana gudana cikin sauki da kwanciyar hankali kuma ma'aikata hukumar zabe sun isa runfunan zaben kan lokaci har ma suka jira masu kada kuri’a.
A yau Laraba ne Michael Cohen, tsohon lauyan Shugaban Amurka Donald Trump, zai koma gaban 'yan kwamitin bincike na majalisar wakilan Amurka don ci gaba da bada shaida.
Wasu rahotanni sun ce Koriya ta Arewa ta sake komawa bakin aikin gina gurin gwada makami mai linzamin, a cewar wasu cibiyoyin bincike na Koriya Ta Kudu da Amurka.
Kasar Pakistan ta ce dakarunta sun harbo wasu jiragen yakin Indiya guda biyu.
Shugaban Amurka Donald Trump da Shugaban Koriya ta arewa Kim Jong Un, sun yi musayar hannu da kuma gaisawa ta jin dadi da junansu, don kaddamar da taron kolinsu karo na biyu.
Hukumar zabe mai zaman kanta a Jihar Plateau, ta gudanar da zabe a runfuna biyu dake kananan hukumomin Jos ta kudu da Riyom anan Jihar Plateau.
Rahotanni sun bayyana cewa wasu 'yan bindiga da ba’a san ko su wanene ba, sun hallaka wasu wakilan zabe a jihar Taraba.
Rahotanni daga jihar Taraba na cewa akwai wasu yankuna na kudancin jihar da ba’a gudanar da zabe ba, lamarin da ya tayar da hankulan al’ummomin yankunan.
Dan takarar babbar jam’iyar adawa ta PDP, kuma tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya kada kuri’ar sa tare da daya daga cikin matansa Titi Atiku Abubakar, a runfar zaben.
Jam'iyyar mai mulki ta kasar Uganda ta amince da shugaban kasar Yoweri Museveni a matsayin dan takara a zabe mai zuwa na shekarar 2021.
Domin Kari