A ranar 19 ga watan Fabrairun wannan shekarar ne mayakan kungiyar Boko Haram suka afka garin Dapchi a jihar Yobe da ke arewa maso gabashin Najeriya, suka sace 'yan mata fiye da 100. Ko da yake, sun dawo da 'yan matan bayan wata guda, amma har yanzu ba a saki wata daliba guda ba mai suna Leah Sharibu.