Babban birnin Somalia Mogadishu, wanda bada dadewa ba ake daukar shi a matsayin birni mafi hadari a duniya, yanzu yana shirin daukar bakwancin taron koli na Hukumar “IGAD” ta Cibiyoyin Raya Kasashen Afrika na 53 a karon farko, a karshen wannan mako biyo bayan yakin basasa da aka kwashe shekaru da dama ana kasar, inji jami’ai.