Wani mai magana da yawun Shugaban Sudan Ta Kudu, Salva Kiir, ya yi watsi da rahoton wani bincike wanda ya zargi Kiir da tsohon Mataimakin Shugaban Kasar Riek Machar, da wawurar dinbin dukiyar kasar, yayin da miliyoyin 'yan Sudan Ta Kudun ke fama da matukar yinwa.