'Yan gudun hijirar kasar Burundi dake wasu kasashe sun ce suna tsoron kisa, da gana azaba daga dakarun gwamnatin kasar idan suka koma.
Majalissar Dinkin Duniya ta ce mutane miliyan hudu da dubu dari takwas ne ke bukatar agajin jinkai a Sudan, kuma yawancin su suna yankin Darfur.
Zaben shugaban kasar da za a yi gobe Alhamis a Kenya shine karo na biyu a cikin wannan shekarar bayan da kotun kolin kasar ta yi watsi da sakamakon zaben da aka yi a baya, ta ce yana cike da magudi.
Ma’aikatar Lafiya a Najeriya ta ja hankalin masu tafiya jinya a kasashen waje da su yi hattara a saboda yadda ake samun rahotannin likitoci masu satar kodar jama'a, musamman a kasar Masar.
Kungiyoyin kare hakkokin bil'adama sun ce an kashe mutane dayawa a lokutan zanga zanga tun bayan zaben shugaban kasa da aka yi a kasar ta Kenya.
Sanarwar da rundunar sojan kasar ta bayar ta ce harkokin tsaro sun koma daidai a birnin na Kirkuk,
Sai dai har yanzu yankunan dake gabashin yankin Deir el-Zour na hannun 'yan kungiyar ta ISIS.
Hukumar lafiya ta duniya ta ce cutar sankara ko daji na cigaba da yin barazana ga rayukan bil’adama a fadin duniya, kasashen Afrika cutar ta fi kamari ciki harda Najeriya.
Rundunar ta bayyana haka ne a taron manema labarai da ta saba gudanarwa duk bayan wata uku wanda aka yi a birnin Yola, jihar Adamawa.
Kakakin gwamnatin kasar Kamaru, ministan sadarwar kasar kuma, Isah Ciroma Bakari, ya yiwa manema labarai jawabi a ofishinsa dake birnin Yaoundé akan rikicin dake faruwa a yankin kasar dake magana da harshen ingilishi.
Gwamnan jihar Neja a Najeriya, Alhaji Abubakar Sani Bello, ya kori yawancin kwamishinonin jihar daga kan mukamansu saboda rashin gamsuwa da kamun ludayin yadda suke gudanar da ayyukan cigaban al’ummar jihar.
Nan take Jami'an Myanmar basu maida murtani akan rahoton na Majalissar Dinkin Duniya ba.
'Yan majalissar dokokin Amurka sun kira tashin hankalin da ya faru a garin Charlottesville aikin "ta'addancin cikin gida".
Wannan ne karo na 12 da dakarun suka kai hari ta sama akan kungiyar mayakan dake Somalia.
Kasashen duniya na ci gaba da caccakar Aung San Suu Kyi saboda rikicin dake faruwa a jihar Rakhine.
Bill Gate ya ce matakan da aka dauka akan nasarorin da aka samu na da muhimmanci matuka.
Harin da aka kai ta sama ya auna wasu motoci guda biyu da 'yan bindigar ke ciki akan hanyar Buula-Banin, A yankin Shabelle
Shahid Khaqan Abbasi, wanda aka nada sabon Firamista, ya dade yana zaman Hadimin tsohon Firayin MInistan Pakistan Nawaz Sharif.
Mataimakin shugaban Amurka Mike Pence ya ce dole ne Rasha ta canza Idan tana So a dage mata takunkumin da aka sanya ma ta.
Shugabannin kungiyoyin adawa na kasar Venezuela na zargin shugaba Maduro da niyyar zama shugaban kama-karya idan har aka yi zaben wakilan da zasu rubuta sabon kundin tsarin mulki da ya ke so.
Domin Kari