Wannan dokar zata taimakawa wadanda aka shigo da su Amurka tun suna kanana, basu san wata kasa sai ta Amurka.
Shirin dokar ya ba 'yan majalissar tarayyar Amurka damar kin amincewa da sassauta takunkumin da za a sa akan kasashen.
Tun bayan da kasar Isra'ila ta sanya tsauraran matakan tsaro a wurin Masallacin al-Aqsa, Musulmai a birnin Kudus suka fara nuna bacin ransu ta yin Sallah a wajen Masallacin.
Wasu jami'an gwamnatin Amurka sun ce matakin na zaman wani bangaren kokarin gyara dangantakar dake tsakani Amurka da Rasha.
Kumburin da likitoci suka gano a cikin kwakwalwar Sanata Johan McCain na jam'iyyar Republican na tattare da illa.
Shugaba Trump ya sha nanata cewa babu wata alaka tsakanin kwamitin kamfen dinsa da jami'an Rasha.
Har yanzu manyan jami'an fadar White House ba su bada cikakken bayanin hirar da Trump da Putin suka yi.
Sakataren harkokin wajen Amurka bai amsa tambayoyi ba game da ganawarsa da sarkin Qatar.
Sabanin rahotannin dake nuna cewa Putin ya taimakawa Trump cin zabe, shugaban na Amurka ya ce Rasha ta so a ce Hillary Clinton ce ta lashe zaben.
Bayan ganawa da takwaransa na kasar Faransa Emmanuel Macron, shugaba Donald Trump zai kuma halarci bikin Ranar Kasa a birnin na Paris.
Kamfanin jiragen saman Qatar da tashar jirgin saman kasa-da-kasa ta Hamad sun cika sabbin ka’idodin tsaro da Amurka ta gindaya.
Maharan sun tsare daruruwan mutane, ciki har da 'yan majalisa da 'yan jarida a cikin ginin majalisar kasar har na tsawon sa'o'i tara.
Har yanzu ziyarar da shugaban Sudan Omal al Bashir ya kai Afirka ta Kudu a 2015 na ci gaba da ta da kura, inda a baya-bayan nan, kotun hukunta manya laifuka ta ICC ta zargi Afirka ta Kudu da kin bin ka'idodin da suka rataya a wuyanta.
Shugaban kasar Amurka ya fada a yau Alhamis cewa Amurka da kasashen Turai sun ji jiki daga hare-haren ta’addanci, amma kasashen za su kawo karshen hare-haren.
Shugaban China Xi Jingping na kan wata ziyara a birnin Hong Kong a wani mataki na halarta bikin cikar yankin shekaru 20 bayan mulkin mallaka da Birtaniya ta ma yankin.
A karon farko, an samu wani babba daga cikin makusantar Paparoma Francis a cikin zargin yin lalata a Fadar Vatican. Daya daga cikin abubuwan da Paparoman ya sha alwashin maganacewa a lokacin da ya karbi ragamar jagorancin Vatican shi ne kakkabe wadanda ake zargi da irin wannan laifi.
An saki jami'an Majalisar Dinkin Duniya bayan da wasu 'yan bindigar suka kama su a Libya, kasar dake fama da rikicin siyasa tun bayan da aka hambarar da gwamantin tsohon shugaban kasar marigayi Moammar Ghaddafi.
A wani mataki da ba a saba gani ba, kasar Sudan ta Kudu mai fama da rikici ta janye jakadunta daga wasu kasashe bakwai.
Mafi yawancin fasinjojin Iyalan sojojin Kasar ne.
Ministan cikin gidan Faransa Gerard Collomb, ya fadi cewa, mutumin ya furta cewa “harin da ya kai saboda Syria ne”.
Domin Kari