Zababben shugaban Amurka Joe Biden zai yi wani taro a yau Talata domin gabatar da mutanen da yake so ya zaba don rike manyan mukamai na diplomasiyya da na tsaron kasa a gwamnatinsa.
Rahotanni daga Najeriya na cewa wasu daga cikin ‘yan sandan nan da aka yi garkuwa da su a yankin jihar Katsina sun samu kubuta.
Hukumar kwallon Kwando ta NBA a Amurka ta gudanar bikin tantance ‘yan wasan da za su buga wasanni a gasar ta NBA, wanda aka gudanar da shi ta kafar yanar gizo a garin Bristol da ke jihar Connecticut.
A Najeriya, ana ci gaba da laluben hanyoyin da za a iya magance matsalar masu garkuwa da mutane akan hanyar Abuja zuwa Kaduna bayan wani mummunan harin da ‘yan bindiga suka kai a baya-bayan nan.
Najeriya na ganin dishi-dishi a kokarin da take yi na neman gurbin shiga gasar cin kofin nahiyar Afirka da za a yi a badi.
Rahotanni daga kasar Masar na cewa dan wasan kungiyar kwallon kafa ta Liverpool Mohammed Salah ya kamu da cutar COVID-19.
Jami’an zabe a jihar Georgia da ke Amurka sun fara aikin sake kidaya kuri’un da aka kada a sassan jihar 159 a zaben shugaban kasar da aka yi a makon da ya gabata - amma wannan karon da hannu.
Bayan kwanaki da aka kwashe jama'a na tsokaci dangane da hotunan da jarumar Rahama Sadau ta wallafa wadanda suka bakanta ran al'umar Musulmi, jami'an tsaro na neman jarumar ta fim din "Mati A Zazzau."
Babban Atoni Janar din Amurka William Barr ya ba masu shigar da kara na gwamnatin tarayya umurnin su binciki “tarin zarge-zarge” da ake yi kan tafka magudi a zaben shugaban kasar da aka yi a makon da ya gabata, matakin da ya sa daya daga cikin jami’in ma’aikatar shari’ar ya ajiye aikinsa.
Gwamnan jihar Legas da ke kudu maso yammacin Najeriya, Babajide Sanwo-Olu, ya bayyana aniyarsa ta soke dokar nan da ta ba da damar a rika biyan tsoffin gwamnoni da mataimakansu kudaden fansho.
Ana shirin ci gaba da sauraren kara kan tsarin kiwon lafiya mai rahusa da 'yan Republican suke adawa da shi a Kotun Kolin Amurka.
Ratar da dan takarar jam’iyyar Democrat Joe Biden ya ba shugaban Amurka Donald Trump a kidayar kurin’n da ake yi a jihar Pennsylvania ta kara fadada.
Dan takarar jam’iyyar Democrat Joe Biden ya kara kusantar yiwuwar samun nasarar lashe zaben shugaban Amurka yayin da alkaluman da aka sabunta suka nuna ya tserewa Shugaba Donald Trump a jihohin Georgia da Pennsylvania.
'Yan takarar shugabancin Amurka duka biyu, kowannensu na ikirarin shi ya lashe zaben.
Zaben Amurka na neman barin baya da kura, inda ake samun mabanbantan ra'ayoyi.
Rahotanni daga birnin N’Konni a Jamhuriyar Nijar na cewa, wani Ba’amurke da aka sace a kasar aka tsallaka da shi arewacin Najeriya ya samu kubuta.
Fitaccen jarumin nan dan asalin kasar Scotland Sean Connery, wanda ya samu daukaka da fina-finan “James Bond” cikin gomman shekaru da ya kwashe yana harkar fim, ya rasu. Shekararsa 90.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ya kira tsoffin shugabannin kasar wani taron gaggawa don tattauna halin da kasa ke ciki.
Matasa a wasu jihohin Najeriya, sun yi ta afkawa rumbunan adand abincin tallafin da gwamnati ta tanada don ragewa mutane radadin annobar coronavirus da ta addabi duniya.
Shugaban Amurka Donald Trump da ke takara karkashin jam’iyyar Republican, ya kada kuri’arsa a Florida a zaben shugaban kasa da za a yi na ranar uku ga watan Nuwamba.
Domin Kari