Shugaban Turkiyya, Recep Tayyib Erdogan, ya fadi yau Litini cewa ya kamata duniya ta mutunta nasarar da jam'iyyarsu ta Adalci da ci gaba ta samu a zaben majalisar dokokin da aka gudanar, wanda ya bayyana da cewa zabin kwanciyar hankali mutanen kasar ta Turkiyya su ka yi.