A Jihohin Kano da Jigawa An samu isar Jami’ai da kayayyakin zabe da wuri a wasu mazabu na yankunan jihohin.
Dazu da maraice shugaban Najeriya ya kammala ziyarar yakin neman zabe a Kano, sai dai shugaban bai yi wani sabon alkawari ba musamman ta fuskar lamuran da suka shafi farfado da masana'antun Kano da harkokin kasuwanci.
An kammala taron masu ruwa da tsaki kan harkokin noman Tumatir na kasa a jihar Kano, inda aka tattauna game da maradu da kuma kalubalen da manoman Tumatir ke fuskanta a Najeriya.
A yayin laccar neman kuri'a a Dutsen jiahr Jigawa, dan takarar jam'iyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar ya yi alkawarin inganta rayuwar talakawa ta wajen samar da ayyukan yi, da bunkasa noman rani
Wani rahoton Majalisar Dinkin Duniya ya nuna cewa muddin Najeriya ba ta dauki matakan daya dace ba, akan harkokin tattalin arziki nan da shekara ta 2050, kasar za ta zama daya daga cikin mafi talauci a duniya.
Yayin da jam'iyyu da 'yan sisaya a Najeriya ke ci gaba da yakin neman zabe domin tunkarar babban zaben kasar da za'ayi a watan gobe, Jam'iyyar hamayya ta PDP a jihohin Jigawa da Neja tace ta daura damarar dawo da gwamnati a wadanndan jihohi.
Wasu Dattawa a jihar Kano sun yi kira da babbar murya ga gwamna Abdullahi Umar Ganduje da ya fito yayi wa mutanan kano bayani akan faifan bidiyo da ake zargin ya nuna shi yana karbar cin hanci daga gurin yan kwangila.
Batun takaddama tsakanin gwamnatin Najeriya da kungiyar Malaman Jami'o'in kasar na ci gaba da haifar da damuwa ga dalibai da sauran masu ruwa da tsaki a sha'nin ilimin.
Hukumar kula da Kamfanonin sadarwa ta Najeriya wato NCC ta ce 'yan kasar fiye da miliyan 160 suka mallaki layin wayar salula, yayin da sama da miliyan 90 ne daga cikin su ke amfani da fasahar sadarwa ta intanet.
Kimanin shekaru biyar bayan kafuwarta, Jami’ar Sule Lamido dake garin Kafin Hausa a jihar Jigawa, ta yaye rukunin farko na dalibanta su 332 har ma gwamnan Jigawa Badaru Abubakar yace gwamnatin Jihar zata ci gaba da daukar matakan bunkasa Jami’ar.
Masana da kwararru kan harkokin tsaro a ciki da wajen Najeriya ,da malamai da kuma sarakunan gargajiya suna halartar wani taron wuni uku kan matsalar yakin sari ka noke da tarzomar mayakan Boko Haram a Najeriya.
Da alama, aikin binciken da majalisar dokokin Kano ke yi kan zargin karbar na goro daga hannun ‘yan kwangila na dala miliyan biyar a kan gwamnan jihar Abdullahi Umar Ganduje ya samu koma baya, bayan da babbar kotun jihar ta bada umurnin dakatar binciken har sai ta kammala sauraren karar gabanta.
Masana harkokin siyasa sun nuna damuwa dangane da abinda suka bayyana a matsayin dutsen tuntuben siyasa da ya shafi jingina ga masu hali ko ikon fada aji a tsarin damokaradiya.
Rashin samun ‘yancin karbar kudaden kai tsaye daga asusun tarayya, na ci gaba da kasancewa babbar kalubala wajen tafiyar da harkokin mulki da shugabanci a matakin kananan hukumomi a Najeriya.
Majalisar dokoki ta jihar Kano tace gwamna Abdullahi Umar Ganduje tare da dan kwangilar da ake zargin ya bashi toshiyar baki da kuma mawallafin Jaridar data buga batun zasu gurfana a gaban kwamitin data kafa domin bincikar lamarin
Yayin da siyasa ke dada zafi saboda shirin zabe da ke tafe a 2019, wasu faya-fayen bidiyo sun bullo masu nuna kamar Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na jahar Kano na amsar na goro daga wasu 'yan kwangila.
Jam’iyyun siyasa a Najeriya na ci gaba da gudanar da zabukan cikin gida domin fitar da ‘yan takarar mukamai daban-daban a babban zaben kasar da aka shirya gudanarwa cikin watan Fabarairun badi.
A cikin wannan mako ne hukumomi a kasar India suka ayyana wata doka datayi tanadin daurin shekaru uku a kurkuku ga duk magidancin daya yiwa matar sa saki uku a jere lokaci guda a wani mataki na rage sakin aure barkatai a fadin kasa.
Domin Kari