Wata kotu a Uganda a ranar Talata ta yi watsi da bukatar da wata kungiya mai fafutukar kare hakkin bil adama ta LGBT ta shigar da ke neman tilasta wa gwamnati yin rajista, in ji lauyan mai shigar da kara.
A ranar Litinin din da ta gabata ne sojojin Najeriya suka fara farautar wasu masu garkuwa da mutane da suka yi awon gaba da daliban makaranta kusan 300 a jihar Kaduna kamar yadda wata majiyar tsaro ta bayyana, yayin da iyayen dake cikin rudani suka bukaci a sanar da su lokacin sake haduwa da yaransu
Masu aikin ceto a tekun kasar Spaniya sun ce sun ceto mutane 38 da ransu tare da samun gawarwakin wasu biyu daga cikin wani kwale-kwalen bakin haure da ya taso daga yammacin Afirka ya ke kokarin isa tsibirin Canary.
Akalla mutane 50 ne suka jikkata a ranar Litinin, akasarinsu da kananan raunuka, bayan da kamfanin jirgin LATAM ya shaidawa jaridar New Zealand Herald cewa ‘tangardar na'ura’ ta sabbaba wani ‘kwakkwaran motsi’ a tafiyar wani jirgin sama daya tashi daga birnin Sydney zuwa Auckland a kasar Australia.
Aljeriya na shigo da naman sa da na rago mai tarin yawa domin tunkarar yanayi bukatu na naman da ake sa ran amfani da shi a duk watan Ramadan mai alfarma, tare da fatan daidaita farashin yayin da tattalin arzikin kasar ke ci gaba da kokawa.
Falasdinawa sun fara azumin watan Ramadan kamar sauran dauniya ne a yau Litinin a daidai lokacin da watan na Mususlmi ya fara kuma babu wata tattaunawar tsagaita wuta.
Hira da wata mai fafutuka akan albarkacin zagayowar ranar mata ta duniya; a birnin Jos na Najeriya wata mata ta dukufa koyawa mata sana’o’i da karfafa su don ganin sun iya shawo kan kalubalen da zai iya hana su cimma muradunsu, da wasu rahotanni
IWD rana ce ta musamman da aka kebe a duniya domin bikin murnar nasarorin zamantakewa, tattalin arziki, al'adu, da siyasa na mata.
Ministan harkokin wajen Najeriya Yusuf Maitama Tuggar da takwaransa na Rasha Sergey Lavrov sun tattauna batutuwan da suka shafi moriyar juna da kuma zaman lafiyar yankin a birnin Moscow ranar Laraba.
Babban jami’in ‘yan gudun hijira na Majalisar Dinkin Duniya ya yi wani sabon gargadi yau Alhamis cewa sama da mutane 780,000 suka rasa matsugunansu a Mozambique, mafi yawansu saboda tada kayar baya na tsawon shekaru bakwai da kungiyar jihadi ta yi wanda ya jefa arewacin kasar cikin rudani.
Domin Kari