Hukumomin Jamhuriyar Nijar sun bada sanarwar sake bude iyakokin kasar da nufin baiwa jama’a damar zirga-zirga a tsakanin kasar da kasashe makwafta amma da sharadin nuna takardar shaidar gwajin cutar COVID-19.
Kungiyar Amnesty International ta bukaci gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta dauki matakin baiwa dan gwagwamaryar nan Anas Djibrilla damar ganawa da lauyansa bayan da ya shafe watanni kusan 3 a garkame a gidan kason Koutoukale saboda zarginsa da yunkurin kifar da gwamnati.
kungiyar ROTAB mai fafutukar ganin an yi haske a sha’anin ma’adanan karkashin kasa ta bukaci gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta dauki matakan da za su bada damar rajistar mutanen da ayyukan shimfida bututun man Nijar-Benin zai raba da gonakinsu don ganin ba a manta da kowa ba wajen biyan diyya.
Hukumomin kasar sun ce sun rufe kafar sada zumuntar ce, saboda tana barazana ga zaman lafiyar Najeriyar, la'akkari da irin sakonnin da take bari ana wallafawa.
Majiyoyi sun ce daga cikin mutanen da aka kubutar har da ma'aikatan agaji, wadanda kungiyar ta Boko Haram ta sace su a shekarar da ta gabata.
A yayin da ake shirin bikin tunawa da zagayowar ranar yaran Afrika ta 16 ga watan Yuni wata kungiyar kula da kare hakkin yara kanana CONAFE Niger da kungiyar MDM ta kasar Belgium, sun shirya wani taro domin horar da likitoci dubarun baiwa yara kariya daga annobar covid 19.
A ci gaba da hauhawar kazancewar tsaro a kusan duka sassan Najeriya, babban titin Abuja da ya tashi daga Kaduna zuwa Zariya da kuma garuruwan dake zagaye da yankin da birnin na Zazzau mai dimbin tarihi da muhimmanci a halin yanzu dai na cikin firgici
Ana ci gaba da samun masu kamuwa da cutar corona a Najeriya a daidai lokacin da ake ci gaba da rigakafi da wayar da kan jama'a kan hanyoyin kare kai da kai.
Hukumomin kiwon lafiyar al’uma a Jamhuriyar Nijar sun shirya wani babban gangami da nufin karrama ranar masu bada jini ta duniya wacce ake shagulgulanta a ranar 14 ga watan Yuni a ko ina a duniya da nufin ganar da jama’a mahimmancin bada gudunmowar jini a asibitoci.
A cikin Shirin na wannan makon yayin da ake ci gaba da samun hadarin jiragen ruwa a wasu sassan Najeriya, wasu al’ummomi a jihohin Kebbi da Sokoto sun bukaci gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki da su sa hannu don kawo karshen asarar rayuka da dukiyoyi, da wasu sauran rahotanni.
Taron wanda ya gudana a babban birnin tarrayar Najeriya na Abuja, ya tabo batutuwa da dama da suka bayyana halin kunci da al’ummar Fulani ke fuskanta a fadin kasar a cewar shugaban kungiyar ta kasa Alhaji Muhammadu Kiruwa.
‘Yan Nijar kamar sauran takwarorinsu na kasashen Afrika renon Faransa sun fara maida martani bayan da shugaba Emmanuel Macron na Faransa ya bayyana shirin janye sojan kasar daga yankin Sahel.
Hukumar yaki da fataucin miyagun kwayoyi OCRTIS a Jamhuriyar Nijar ta shigar da kara a kotu bayan da wata jarida mai zaman kanta dake da ofishi a kasar Switzerland ta ruwaito wani labari dake cewa wani bangare na tabar wi-wi da aka kama a Nijar a watan Maris din da ya gabata ya koma wajen mai shi.
A cikin shirin na wannan makon tun bayan da shugaban kasar Najeriya ya sanar da nadin Manjo Janar Farouk Yahaya a matsayin sabon babban hafsan sojin kasar, ‘yan kasar ke ci gaba da tsokaci a game da irin aikin dake gaban sabon babban hafsan sojin, musamman batun Boko Haram da wasu sauran rahotanni.
Kasa da kwana goma da kifewar jirgin ruwa wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutum sama da 100 a jihar Kebbin Najeriya, an sake samun hatsarin wani kwale-kwale a jihar Sakkwato wanda ya yi sanadin mutuwar mutum 13.
Tawagar jami’an hukumar kare hakkin dan adam ta kasar Burkina Faso, ta kai ziyara Nijar da nufin karawa juna sani sakamakon abinda aka kira jajircewar hukumar kare hakkin dan adam ta Nijar wato CNDH wajen fito da sahihan bayanan cin zarafi da toye hakkin jama’ar kasar ba tare da nuna son rai.
A Jamhuriyar Nijar, ‘yan kasar sun yaba da nasarorin da sojojin kasar suka fara samu da hadin gwiwar takwarorinsu na rundunar MNJTF a yakin da suke gwabzawa da ‘yan ta’adda.
Domin Kari