Shugabannin harkokin kasuwancin kasar Birtaniya suna kara gabatar da bukatocinsu da suka shafi ficewar kasar daga Kungiyar Tarayyar Turai-KTT, yayinda suke kokarin amfani da sakamakon zaben da aka gudanar makon da ya gabata, da ya raunana jam’iyar Conservative ta Theresa May, da ta gaza samun rinjaye kai tsaye a majalisa.