Mazauna kauyukan Tungar Kafau, da Mallamawa, da Shinkafi da wasu kauyuka a jihar Zamfarar Najeriya suna cikin zaman fargaba sakamakon wasu hare haren da wasu yan ta’adda suka kai musu tsakanin kwanaki biyu, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutane kusan hamsin a wadannan kauyukan a Zamfara.