Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Hukumomi sun dauki sababbin matakan tsaro Abuja babban birnin kasar


Harin bom a babban birnin tarayya Abuja.
Harin bom a babban birnin tarayya Abuja.

Hukumomi a Najeriya sun dauki sababbin matakan tsaro a Abuja babban birnin kasar bayan kazamin harin bom da aka kai a shelkwatar ‘yansandan kasar.

Hukumomi a Najeriya sun dauki sababbin matakan tsaro a Abuja babban birnin kasar bayan kazamin harin bom da aka kai a shelkwatar ‘yansandan kasar. Jami’an gwamanati a babban birnin kasar sun bayyana matakan tsaron da za a dauka a wuraren da jama’a da dama ke taruwa, a wata sanarwa da suka bayar yau Laraba. Yanzu an bukaci gidajen barasa da gidajen silma dake birnin tarayya Abuja su rufe da karfe goma na dare. Yayinda za a rufe wuraren da kananan yara ke taruwa da suka hada da wuraren wasan yara da filayen shakatawa su rufe da karfe shida na yamma. Hukumomi sun kuma hana ajiye motoci a kan wadansu manyan hanyoyi biyu inda ofisoshin gwamnati suke. Jami’ai a birnin tarayya Abuja sun ce daukar wadannan matakan ya zama tilas domin tabbatar da kare kaddarorin gwamnati.

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 3:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG