Yawan gallaza ma jama'a da ake zargin 'yan sanda na musamman da ake kira SARS da yi, ya sa wasu matasa yin zanga zanga a gaban ginin shelkwatar ‘yan sanda da ke birnin tarayyar Najeriya, Abuja.
Tsohon dan takarar shugaban kasar Mali Soumaila Cisse ya gana da shugaban rikon kwaryar kasar a daren ranar Alhamis 8 ga watan Oktoba karon farko tun bayan sakinsa a wannan makon da masu kaifin kishin Islama suka yi a wata musayar fursunoni.
Yayin da dalibai su ka koma makaranta da tsarin karatu kusan irin wanda aka saba da shi, masu lura da al'amura na ganin da alamar ba a dau ingantattun matakan kare dalibai ba a jahar Kebbi.
Yayin da masu kai ziyarar ibada ta mabiya tafarkin Mouride ke ta dunguma zuwa birni mai tsarki na Touba a kasar Senegal don ayyukan ibada na Magal, hukumomi na damuwa kan yiwuwar hakan ya yada cutar corona.
Hukumar NCDC mai kula da cututtuka masu yaduwa a Najeriya ta ce an samu karin mutum 120, da suka kamu da cutar COVID-19 a ranar Litinin, 05 ga watan Oktoba.
Bayanai na nuna cewa rashin cancantar daliban jahar Kano ta Najeriya ya haifar da tafiyar hawainiya ga kwalejin gamayya ta Jamhuriyar Nijar da jahar Kano ta Najeriya.
A cigaba da rigimar da ta biyo bayan wasu kalaman da tsohon Mataimakin Babban Bankin Najeriya, Dr. Obadiah Mailafiya ya yi game da matsalar tsaro a Kudancin Kaduna, wata kotu a Jos ta tabbatar da hurumin hukumar 'yan sandan da ta gayyace shi
Amurkawa sama da miliyan 100 ake kyautata zaton za su kalli muhawarar farko tsakanin Shugaba Donald Trump na jam'iyyar Republican da Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa Joe Biden na Jam'iyyar Demokarat.
Wata sabuwa kuma ta kunno kai game da takarar sanannen dan adawar Jamhuriyar Nijer dinnan, Hama Amadou. Wannan karon takaddama ake yi kan rashin rajistarsa.
Jama'a sun yi cincirindo tare da daukar matakan kandagarki a wurin nadin sabon Sarkin Biu, Mai Martaba Mustafa Umar Mustafa.
A cikin wani hali na juyayi da alhini, an yi jana'izar marigayi Kanar Dahiru Ciroma da wasu 'yan bindigar da ake kyautata zaton 'yan Boko Haram ne su ka kashe shi yayin da ya ke wani sintirin tabbatar da tsaro a Danboa, jahar Borno.
Kasar Saudiyya ba ta kau da yiwuwar kulla dangantaka da kasar Yahudu ba, to amma ta ce sai kasar ta Isira'ila ta daidaita da Falasdinawa tukun.
A wani al'amari mai janyo takaddama da fassari iri iri, wato kotu a China ta yanke ma hamshakin mai kudin nan kuma dan siyasa, Ren Zhiqiang daurin shekaru 18 a gidan yari.
Cibiyar Yaki Da Cututtuka Masu Yado Ta Amurka ta janye wani karin bayanin da ta yi ranar Jumma'a kan yadda cutar corona ke yaduwa. Ta ce ana bukatar kara tantance bayanin.
Ta leko ta koma ga batun sake bude makarantu a Janhuriyar Nijer ganin yadda ambaliyar ta hana, bayan dan sassaucin da ake ganin an dan samu game da annobar cutar corona, wadda ta sa aka dage tun farko.
Kamar yadda aka saba a duk lokacin da aka yi rashin iyayen kasa, dinbin mutane sun yi cincirindo wajen jana'izar Mai Martaba Sarkin Biu, Mai Umar Mustapha Aliyu, duk kuwa da wannan marra da ake ciki, saboda nuna girmamawa da kuma alhini.
Domin Kari