A Jamhuriyar Nijar, jiya Alhamis, 15 ga watan Satumba, aka yi shagulgulan baje kolin al’adun al’ummar Tubawa bayan da a shekarar 2020 shugabanin wannan kabila dake zaune a kasashen Nijar, Libya, da Chadi suka yanke shawarar ware ranar.
Ambaliyar ruwan da ake fuskanta a sassan Nijer sanadiyar ruwan saman da ake yi ta haddasa asarar rayukan mutane fiye da 100 sannan ta yi sanadin hasarar dimbin dukiyoyi, lamarin da ya sa gwamnatin Nijer soma neman gudummowar abokan hulda na kasa da kasa don agaza wa wadanda bala’in ya rutsa da su.
Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta kaddamar da wani shirin hadin gwiwa da Bankin Duniya mai lakanin “Haske” da nufin samar da wutar lantarki da makamashi a daruruwan garuruwan kasar.
Shugaban gwamnatin rikon kwaryar Burkina Faso Paul Henri Sandaogo Damiba ya kai ziyara a Jamhuriyar Nijer da nufin neman hanyar shawo kan matsalolin da su ka addabi yankin.
A Nijr, an gudanar da bikin kaddamar da ayarin zaman lafiya inda cibiyar fina-finai ta CINE NOMADE da tallafin ofishin jakadancin Amurka a Nijar za ta zagaya jihohin kasar da nufin tattaunawa da jama’a akan batun zaman lafiya musamman matasa.
Kungiyoyin da ke ayyukan waye kan jama’a a game da illolin ta’ammali da miyagun kwayoyi sun bayyana damuwa dangane da yadda al’amarin ke kokarin samun gindin zama a ‘yan shekarun nan a Nijar.
Taron na zuwa ne a wannan lokaci da masu ta da kayar baya ke fakewa da addini don jan ra’ayin jama’a.
Mukaddashin Mataimakin Karamin sakataren gwamnatin Amurka mai kula da sha’anin tsaron kasa da kasa Gonzalo Suarez ya bayyana gamsuwa da kyakkyawar fahimtar da ke tsakanin Amurka da jamhuriyar Nijar a yakin da suka kaddamar da nufin murkushe aikin ‘yan ta’adda a yankin Sahel
Hankulan mazauna yankunan karkara a Jamhuiryar Nijar ya fara kwantawa bayan da ma’aikatar hasashen yanayin kasar ta kaddamar da ayyukan harbin giza-gizai domin samar da wadatar ruwan sama musamman a yankunan da aka fuskanci barazanar fari a watan yulin da ya gabata.
Kungiyar agajin gaugawa ta kasa da kasa ICRC ta yi bayani a game da girman matsalar bacewar al'umma a Nijer tare da jan hankulan jama’a a game da hanyoyin bi don gabatar da koke a ofisoshinta a duk lokacin da wani makusanci ya yi batan dabo.
Hadin gwiwar kungiyoyin fafutuka na Tournons La Page na Jamhuriyar Nijar ya shawarci daukacin kungiyoyi masu zaman kansu su fara aiki da tsari na kayyade wa’adin shugabanci.
Yau ake bukin tunawa da ranar Hausa ta duniya da nufin bunkasa harshen Hausa da al’adun bahaushe sakamakon lura da tasirin Hausa a zamantakewar al’umomin kasashen da ke amfani da ita a matsayin hanyar sadarwa da musanyar abubuwa da dama.
A yayin da farashin ababen masarufi ke kara tashi a Jamhuriyar Nijar kwamitin ministocin da ke kula da yaki da tsadar rayuwa ya kira taron manema labarai domin sanar da al’umma yunkurin da gwamnati ke yi don tunkarar wannan al’amarin.
Gwamnatin Jamhuriyar Nijer ta gargadi direbobin tasi da masu manyan motocin jigila su mutunta dokar da ta kayyade kudin motocin haya ko kuma su fuskanci fushin hukuma.
Masu motocin jigilar fasinja da masu motocin dakon kaya sun cimma wata yarjejeniya da hukumomin jamhuriyar Nijer don ganin karin farashin man diesel din da aka yi a kasar a makon jiya bai shafi kudin motocin haya ba.
Matakin na zuwa ne a wani lokacin da al’ummar ta Nijar ke fama da tsadar kayan abinci saboda haka kungiyoyin fafatukar ke cewa suna jiran su gani a kas domin ba zasu laminci dukkan wani matakin da zai kara wa talaka damuwa ba.
Yayin da 'yan Najeriya ke ta cece kuce kan kudin da aka sayo motocin da aka bai wa Nijar da su ke ganin akwai coge a ciki, su kuwa 'yan Nijar damuwa su ke yi kan yadda wannan al'amari ya zama abin rigima.
Domin Kari