Gwamnan Jihar Akwa Ibom da ke kudancin Nijeriya, inda rufin wata Majami'a ya fadi akan masu ibada a ranar Asabar da ta gabata, in da mutane da yawa suka mutu, ya bada umarnin kama wadanda suka yi kwangilar ginin, cewar wata kafar yada labarai ta jihar.