Kasafin Kudin shekara 2016 da Shugaba Mohammadu Buhari ya mika wa Majalisar Dokokin Najeriya a watan Disamba da ta gabata, ya zama kasafin kudin farko da aka yi ta jayayya akan sa. Da farko an yi zargin ya bata, sai kuma aka ce an sauya kasafin kudin, daga baya kuma aka ce iri uku daban daban aka gano a majalisar.