Batutuwan da suka shafi, baki ‘yan cirani, diyaucin kasa, da tsaro da kuma makomar tattalin arzikin Birtaniyya sune a zukatan masu kada kuri’a ta farko yau Alhamis a zaben jin ra’ayi na tarihi da kasar ke yi, wadda sakamakon a karshe zai nuna ko kasar zata cigaba da kasancewa a cikin tarayyar Turai ko a’a.