Daliban jami'o'i a Kenya, abubuwan da suke koya sun wuce maganar karatu da lokutan Jarrabawa ko kuma Karatun dare, Wasu shugabannin a Jami’o'i a sun yi zaman ganawa a Nairobi a wannan mako domin tattauna akan batututwa da suka shafi daliban , ciki har da Tashe tashen hankula, Manyan Laifuffuka da kuma wankin-kai da kuma Tsatstsauran ra’ayi.