Gwamnatin jamhuriyar Nijar ta mayar da martani wa kungiyar jami’an kwastam din kasar bayan wani taron gangamin jami’an Kwastam ya nuna rashin amincewa nadin wani jami’in da ba Kwastam ba domin shugabancin hukumar saboda a cewarsu nadin ya sabawa dokar aikin Kwastam.
A Jahar Kano mataimakin shugaban kasar Najeriya Farfesa Yemi Osinbajo, ya jagorancin zauren ganawa da kungiyoyin ‘yan Kasuwa da masu sana’o’i game da shirin tallafawa Jama’a su dogara da kansu na gwamnatin tarayya.
Shirin gwamnatin tarayyar Najeriya na samar wa matasa aiki wanda ake yiwa lakabi da N-Power har yanzu na fuskantar matsaloli.
Majalisar Dinkin Duniya ta ware duk ranar biyar ga watan Disambar kowacce shekara domin tunawa da amfanin ‘kasa a duniya.
Noma Tushen Arziki
Babban kotun tarayyar Najeriya ta bayar da hukuncin a saki Mallam Ibrahim El-Zakzaky cikin kwanaki 45, a kuma bashi diyyar Naira Miliyan 50.
Majalisar Dinkin duniya ta ware duk ranar biyu ga watan Disambar kowacce shekara a matsayin ranar yaki da bauta.
Kasar Iran tayi barazanar mayar da martini bayan da Majilisar dattijan Amurka ta bada umurnin kara tsawaita takunkunmi ta akan kasar ta Iran, domin ko duka ‘yan Majilisar daga jamiyyun kasar sun amince cewa wajibi ne a tabbatar an tilasta yarjejeniyar nan da aka cimmawa da kasar ta Iran.
Zababben shugaban kasar Amurka Donald Trump ya zabi Janar James Mattis mai ritaya a matsayin sakataren tsaro, to amma sai a canza dokar kasa kafin ya iya karban wannan mukamin.
Hedikwatar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce rundunar kai daukin gaggawa dake karkashin ofishin Sifeto Janal na ‘yan sandan kasar ta afkawa gungun wasu masu sace mutane da suka dade suna addabar al’ummar yankin Niger Delta.
Kwana guda bayan kaddamar da shirin gwamnatin tarayyar Najeriya na samar da ayyuka mai lakabi N-POWER jihar Kano na kan gaba a jerin Jihohin Arewa dake korafi dangane da daukar ma’aikata karkashin shirin.
Rasha ta sha alwashi a yau Alhamis cewa zata ci gaba da tallafa ma sojojin gwamnatin Syria a Aleppo har sai an kawar da abinda ta kira ‘yan ta’adda daga birnin.
Gwamnatin tarayyar Najeriya ta fara daukan matasa aiki kamar yadda ta yi alkawali, amma yunkurin ya samu cikas a jihohi da dama a shiyar Arewa mussamman a Jihar Neja da Borno da Adamawa da Katsina da Kano da Kebi da kuma jihar Zamfara.
Yau ne a fadin duniya ake gudanar da gangamin wayar da kan Jama’a game da batutuwan da suka shafi cuta mar karya garkuwan Jikin bil’adama wato HIV/AIDS.
A yau ne shirin gwamnatin Najeriya na samawar da aikin yi ga matasa kimanin dubu 200 ta bangaren koyarwa da harkar gona da kuma bangaren lafiya zai fara aiki.
Majalisar Tsaro ta MDD ta Aiyana zama a yau Laraba domin zabe kan takunkumin da zata sakawa Koriya ta Arewa sakamakon yanke tallafin ta na Makamin Nukiliya da kuma shirin Makamai masu linzami.
Shugaban Amurka mai jiran gado Donald Trump ya fada a yau Laraba cewa zai tsame kansa daga harkokin kasuwancin Kamfanoninsa baki daya, domin ya maida hankali kan aikin shugabancin kasa ba tare da matsala ba.
Bincike ya nuna cewa darajar Naira zata ci gaba da faduwa yayin da kuma daga watan Disamba zuwa farkon shekara mai zuwa za a sami karin farashin kayayyakin masarufi a Najeriya.
Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya shirya zaman tattaunawa na gaggawa a yau Laraba sakamakon karuwar tashe tsahen hankula a Birnin Aleppo dake Arewacin Syria.
Gwamnatin tarayyar Najeriya ta kaddamar da shirin da zai kawo karshen al'adar aurar da 'ya'ya mata kanana.
Domin Kari