A karo na biyu cikin watanni biyu da rabi , an samu rugujewar cibiyar wutar lantarki ta kasa a Najeriya, lamarin da ya jefa jihohi bakwai da babban Birnin Tarayya Abuja cikin duhu.
Shugaba Mohammadu Buhari da yake ziyara a Ingila, yayi Allah wadai da rigingimun da ke faruwa a jamiyyar APC mai mulki, musamman ma batun shugabancin Jamiyyar. Wannan bayani ya fito ne a wata takarda ta musamman da Garba Shehu ya sanyawa hannu.
Shugaban masu rinjaye a majalisar dattawa Sanata Yahaya Abdullahi Abubakar tare da dukkan ‘ya’yan jamiyyar su 70, sun a nuna cewa sarkin yawa ya fi sarkin karfi.
Gwamnan Jihar Neja Abubakar Sani Bello ya shugabanci kwamitin rikon kwarya na Jami'yyar APC a wurin karbar wani rahoto na musamman da Mataimakin Gwamnan Jihar Anambra ya mika wa Uwar Jam’iyya akan rabon mukaman shiyya shiyya.
Hukumar Alhazan Najeriya NAHCON ta umurci hukumomin alhazai na Jihohi su gaggauta fara shirye-shiryen aikin Hajjin bana.
Uwargidan Shugaban Najeriya Aisha Buhari, ta tofa albarkacin bakinta akan cece kuce da ke gudana a kasar sakamakon yin watsi da dokokin da ka iya ba mata damar samun kashi 35 cikin 100 na kujerun siyasa.
Cibiyar Kare Hakkin Masu amfani da wutar lantarki a Najeriya, ta aike wa Shugaban kasa Mohammadu Buhari takarda ta koke akan yadda kamfanonin wutan lantarki suke yawan dauke wuta, musamman a birnin tarayya Abuja.
Majalisar dokokin Najeriya ta gabatar da rahoton sassan da ta yi wa gyaran fuska a kundin tsarin mulkin kasar.
Majalisar Dokokin Kasa ta shirya wata doka da za ta sa ilimin aikin noma ya zama muhimmin darasi a manhajar makarantun sakandare a Najeriya, kamar yadda darasin lisafi da harshen turanci su ke.
A Najeriya, kwararru a fannin shari'a sun mayar da martani akan matakin da Majalisar Dattawa ta dauka na amincewa da kafa karin cibiyoyin horrar da lauyoyi 6 a kasar. A yayin da wasu ke yabawa da yin haka, wasu na cewa siyasa ce kawai.
Kwamitin da ke nazarin gyara kundin tsarin mulkin kasa na majalisar dokokin ya shirya taro da ya gayyato kakakin majalisun jihohin 36 saboda a samu amincewar majalisun dokokin a gyare gyare 51 da kwamitin ya riga ya yi a kundin tsarin mulkin kasar.
Kwamitin sulhu na 'ya'yan jam'iyyar APC da su ka samu sabani sanadiyyar zabukan gundumomi, kananan hukumomi da jihohi, ya bar baya da kura bayan mika rahotonsa ga shugabanin rikon jam'iyyar.
Majalisar Wakilan Najeriya ta kwaranye raderadin da aka yi cewa batun batar bindigogi dubu 178,459 a rundunar 'yan sanda zai wuce salun-alun.
A wannan karon an amince da zaben 'yar tinke, ko ta wakilan jam'iyyu ko ta sulhu amma akwai karin gyara da ya shafi kwarewar 'yan takara.
Wata tirka-tirka da ta kunno kai a kwanakin nan akan batun cire tallafin man fetur, ta sa kungiyar kwadago a Najeriya, zuburar da yan'uwan ta dake jihohi akan yin zanga-zangar lumana, daga ranar 27 ga wannan wata na Janairu da muke ciki.
Korafe-korafe sun kunno kai karara akan halin ko in kula da gwamnatin shugaba Mohammadu Buhari ta ke nunawa, musamman akan batutuwan iri su wa'adin shekaru na yin aiki, ko kuma wa'adin shekarun haihuwa na ma'aikaci da doka ko kundin tsarin mulki ya tanadar.
Mnistan yada labarai Lai Mohammed ya ce Twitter yana tara makudan kudade daga Najeriya ba tare da goyon bayan doka ko bin dokokin kasar ba.
Amma kwararru a fannin siyasa sun ce wannan abu ne mai kamar wuya duba da irin tuhume-tuhumen da ake yi wa Kanu.
Domin Kari