An yi jana'izar mataimakin shugaban kasar Malawi, Saulos Chilima a kauyensa dake kudancin babban birnin kasar a yau Litinin.
Mutane bakwai ne suka mutu yayin da wani jirgin kasan fasinja da na dakon kaya suka ci karo da juna a ranar Litinin a jihar Bengal ta Yamma a Indiya, lamarin da ya lalata karusan fasinja guda uku, in ji 'yan sanda.
Firai Ministan Isra'ila Benyamin Netanyahu ya rusa majalisar zartaswar yakin Isra'ila da aka dorawa alhakin jagorantar yakin Gaza, a cewar jami'an Isra'ila a ranar Litinin.
A karon farko an gano cewa wasu mutane a nahiyar Afirka na amfani da muguwar kwayar Nitazenes dangin opiod, a cewar wani rahoto da kungiyar yaki da manyan laifuka ta kasa da kasa mai zaman kanta da ake kira Global Initiative Against Transnational Organized Crime ta fidda.
Ta yiwu ranar Alhamis kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya zai kada kuri'a kan wani kuduri da Birtaniyya ta gabatar da daftarinsa.
Shugaban Amurka Joe Biden da shugaban Ukraine Volodymyr Zelenskyy za su rattaba hannu kan wata yarjejeniyar tsaro ranar Alhamis, yayin da za su gana a Italiya a gefen taron kolin kungiyar kasashe bakwai masu karfin tattalin arziki a duniya.
Ambaliyar ruwa da guguwa mai karfi sun shafi sassan kudancin jihar Florida da yawa a ranar Laraba, lamarin da ya sa hanyoyi suka cika da ruwa, abinda ya kawo cikas ga ‘yan wasan kwallon hockey na Florida Panthers da ke kan hanyar zuwa gasar cin kofin Stanley da za a yi a Canada.
Wani kwale-kwale da ke dauke da bakin haure ya nutse a yankin tekun Yemen, inda mutane akalla 49 suka mutu, yayin da wasu 140 suka bace, a cewar hukumar kula da baki 'yan cirani ta Majalisar Dinkin Duniya da ake kira IOM a ranar Talata.
Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani ya bayar da umarnin a saki fursunoni 110 daga gidan gyaran hali da ke jihar, a zaman wani bangare na bikin ranar dimokradiyya na bana da kuma murnar cika shekara guda a kan karagar mulki.
Wasu jami’an Amurka biyu sun ce shugaba Joe Biden ne ya amince da matakin tura makaman.
A wani sabon rahoto da ta fidda, kungiyar kare hakkokin bil’adama ta Amnesty International ta bayyana cewa an tsare mata da ‘yan mata ba bisa ka'ida ba an kuma ci zarafinsu a cibiyoyin tsare mutane na sojojin Najeriya bayan da suka tsere daga hannun mayakan Boko Haram a arewa maso gabashin Najeriya.
Mutane 26 ne suka mutu yayin da wasu biyu suka jikkata a wani sabon hari da ‘yan bindiga suka kai kan kauyukan Gidan Tofa da ‘Dan Nakwabo a karamar hukumar Kankara da ke jihar Katsina.
Sojoji na duba tsaunuka da dazuzzuka da ke kusa da wani birni a arewacin Malawi bayan da wani jirgin saman soja dauke da mataimakin shugaban kasar ya bace a yankin a ranar Litinin, in ji shugaban kasar Lazarus Chakwera.
Domin Kari