Wani hari da Isra'ila ta kai ya kashe akalla mutane tara a birnin Khan Younis da ke kudancin Gaza, a cewar jami'an kiwon lafiya na Falasdinu a ranar Talata.
Masu fafutuka a kasar Kenya sun yi kira ga masu zanga-zanga da su sake fitowa kan tituna a ranar Talata, inda da yawa suka yi watsi da rokon da shugaban kasar William Ruto ya yi na a tattauna bayan matakin da ya dauka na janye shirin kara haraji.
Jami’ar hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Ogun, Omolola Odutola, ta tabbatar da sace wani direba da wasu mutane dauke da makamai suka yi a hanyar Ijebuode/Sagamu.
A cewar kwamishinan, mai yiwuwa maharan sun yi amfani ne da kan iyakokin jihar da babu tsaro wajen kai hare-haren.
Yayin da Trump da Biden za su sake karawa a zaben bana dukkansu sun tabo batun tashin hankalin 6 ga watan Janairun 2021 a yakin neman zabensu; Wasu manoma a jihar Neja dake arewacin Najeriya su na korafin cewa gwanmati ta kwace filayen su ne da karfi ba tare da diyya ba, da wasu rahotanni
'Yan sandan Kenya sun harba barkonon tsohuwa kan masu zanga-zanga da dama tare da toshe titunan hanyar zuwa fadar shugaban kasar a ranar Alhamis, yayin da ake ci gaba da gudanar da kananan zanga-zanga a garuruwa da dama.
Domin Kari