Kamfanin Mai na Najeriya NNPC ya kulla wata yarjejeniya da wasu Bankuna na kasashen waje, da zata taimaka wajen inganta harkokin Man fetur da iskar Gas da kasar ke da su.
Hukumar NAFDAC mai kula da inganci abinci da magunguna ta Najeriya ta kama kwalaben magungunan tari kimanin miliyan biyu da rabi, bayan da gwamnati ta haramta sayar da duk magungunan tari dake dauke da sinadarin Codeine.
Kasa da sa'o'i 24 da ganawar da Shugaba Buhari yayi da takwaransa na Benin Patrice Talon inda suka duba batun magance matsalar fasa kwori musamman na shinkafa da ake yi tsakanin kasashen biyu.
A yayinda jam’iyar PDP ke ci gaba da murna da kuma shagali bisa sauya sheka da wasu yan majalisar dattijai da wakilai sukayi daga jami'iyar APC mai mulki, rashin komawan yayan jam’iyar APC daga yankin kudu maso yammacin Najeriya zuwa PDP ya kara nuna alamun cewar jam’iyar PDP bata da karbuwa a yankin kudu maso yanmacin najeriya
Majalisar Dinkin Duniya (MDD) ta ware duk ranar 18 ga watan Yuli a matsayin ranar tunawa da Nelson Mandela, shugaban Afirka ta Kudu kuma wanda yayi rajin neman ‘yancin bakaken fata.
An kamala wani taron kasa da kasa domin inganta adabin baka na yankin nahiyar afrika, taron da kungiyar raya adabin baka ta duniya ta dauki nauyin gudanar dashi a birnin Lagos.
Kokarin da kungiyar raya kasashen ketare da gwamnatin Amurka ke yi na tallafawa Najeriya ta zama mai dogaro da kai ta fuskar abinci, hukumar USAID ta shirya taron bita ga wasu malaman bangaren noma na jami’oin Najeriya domin samun nasarar shirin.
A yau Laraba ne shugaban Faransa Emmanuel Macron ya ke kammala ziyarar daya kai Najeriya domin habaka huldar tattalin arziki da Al’adu tsakanin Kasashen biyu.
‘Yan Najeriya naci gaba da tofa albarkacin bakunan su game da cancanta ko rashin cancantar mataki na gwamnatin tarayyar Najeriya ta dauka na karrama Cif MKO Abiola da ake ikirarin ya lashe zaben shekara ta dubu da dari tara da casa'in da uku
Matsalar tattalin arziki a Najeriya ya ragewa kasuwar China Town dake birnin Legas armashi.
Gwamnatin Najeriya ta fara aiki da sabon haraji da ta saka wa kamfanonin tabar sigari da na barasa abin da kuma ke samun martani daga jama'ar kasar.
Wasu gungun likitoci a Najeriya sun kirkiro wata mahajar da za ta rage cinkoso ko tsawon lokutan ganin likita a Najeriya.
Wata kungiyar al’ummar ‘yan arewacin Najeriya dake zaune a kudancin kasar ta gudanar da taron zaman lafiya tare da nuna rashin jin dadi game da tabarbarewar tsaro a kasa baki daya.
Tsakanin Najeriya da sauran kasashen duniya ana asarar biliyoyin dalar Amurka, sakamakon ayyukan ‘yan damfara da aka fi sani da ‘yan 419, ko Yahoo-yahoo Boys.
A yayin da gwamnatin Jihar Legas ke barzanar rufe mayankar da ke Agege, mahauta da dillalan shanu sun yi barazanar daina kai shanu Jihar, lamarin da ka iya haifar da karancin nama.
Majalisar Dinkin Duniya ta ware duk ranar 25 ga watan Afrilu na kowacce shekara domin yaki da cutar zazzabin cizon sauro da ake kira Malaria.
Rundunar ‘yan sandan jihar Legas ta kama wasu tarin makamai da alburusai kimanin 400 a cikin watanni shida, a wani yunkuri na raba al’umma da makamai gabanin zaben 2019.
An kammala wani babban taron habaka harkokin kasuwanci da kudi na musulunci da aka gudanar tare da hadin gwiwar ma’aikatar kudi ta Najeriya, wanda kungiyar habaka masana’antu masu zaman kansu a nahiyar Afirka ta shirya a Legas.
Domin Kari