Sa’o’I kafin zaben shugaban kasa na 2023 a Najeriya da aka dade ana jiran gani, Sufeto Janar ‘Yan sandan Najeriya, Usman Baba ya ce har iyau ayyukan ‘yan ta’adda, masu fashin daji da haramtacciyar kungiyar rajin kafa Biafra ta IPOB da reshen ‘yan bindiganta ESN, na ci gaba da zama babban kalubale.