Kasashen Rasha da China da kuma Iran suna nan suna shirya katsalanda a zaben shugaban kasar Amurka da zummar Amurkawa su zabi dan takarar da suke so ya shiga fadar White House, a cewar wani muhimmin kashedi da babban jami’in hukumar yaki da masu liken asiri a Washington.
Adadin kamuwa da cutar COID-19 a fadin duniya na ci gaba da karuwa, inda ya haura sama da miliyan 19 da dubu dari daya, a cewar jami’ar John Hopkins.
Nan da makonni biyu masu zuwa ne ake sa ran dalibai a kasashen nahiyar Afrika ta Yamma zasu fara rubuta jarabawar kammala sakandare.
Matsananciyar guguwar nan da aka yi wa lakabi da “ISAIAS” tana kara ketawa a tsakiyar jihar New York da New England bayan ta hanzarta ratsawa a yankin tsakiyar Atlantika na Amurka, inda akalla ta kashe mutum hudu.
A jiya Talata Sakataren Harkokin Wajen Amurka Mike Pompeo ya yi alkawarin ba da kariya ga masu rajin demokradiyya a Hong Kong wadanda suka tsere daga garin kuma suka la'anci China bayan da Beijing ta ce, an baiwa 'yan sanda umarnin kama masu fafutukar daga ƙasashen waje.
Jami'an Fadar White House da kuma manyan 'yan jam'iyyar Democrat a majalisar dattawa na shirin sake haduwa, bayan da bangarorin biyu sun bayyana samun ci gaba da kokarin su na yin matsaya kan sabon tallafin gwamnati na cutar coronavirus.
An samu wata gagarumar fashewa a tsakiyar birnin Beirut, babban birnin kasar Lebanon da yammacin jiya Talata, lamarin da hallaka mutane sama da 78 kana wasu dubu hudu suka jikkata.
A jiya litinin Fadar White House ta sanar da cewa mai bawa shugaban Amurka shawara kan harkokin tsaro Robert O’Brien ya kamu da COVID-19.
Wurare da yawa da suka samu nasarar farko a yaki da coronavirus, yanzu suna ganin sabbin kamuwa da cutar bayan da suka sassauta dokokin kulle, cikin su har da Vietnam, Australia da kuma Hong Kong.
Bangarorin da ke cikin yarjejeniyar zaman lafiyar Sudan ta Kudu sun kasa cimma wa’adi na yankin da aka basu ranar Lahadi da ta gabata da su rushe da kuma sake fasalin majalisa.
Mai nazarin harkokin mulki a kasashen Afrika farfesa Boube Na Mewa na jami’ar Diof dake Dakar, Senegal ya bayyana cewa, yunkurin kasashen ECOWAS na warware rikicin kasar Mali tamkar kitso ne da kwarkwata.
Hukumar dakile yaduwar cututtuka a Najeriya, (NCDC), ta fitar da alkalumma a kan yakin da take yi da yaduwar COVID-19 a wani sakon Twitter a jiya Litinin.
A jiya Litinin ‘yan majalisa dokokin Amurka suka koma Washington, inda suke fuskantar tattaunawa mai muhimmanci tare da shugaban kasa Donald Trump.
Allurar rigakafi coronavirus da masana kimiyya suka samar a jami’ar Oxford ta nuna yadda ta ke da tasiri wurin kare garkuwar jiki.
Domin Kari