Mata sun gudanar da gagarumin gangami jiya asabar a birane daban daban na fadin kasar da nufin karfafawa Amurka guiwa su fita zaben shugaban kasa da za a gudanar ranar uku ga watan Nuwamba.
Jiya Lahadi shugaban Amurka Donald Trump da mai kalubalantarsa na jam’iyyar Democrat Joe Biden suka yi zawarcin masu jefa kuri’ar farko a jihohin da ake fafatawa jihar Nevada da North Carolina, yayin da muhawarar karshe ta shugaban kasa ke karatowa a wannan makon.
Sufeto Janar na ‘yan sandan Najeriya ya yi karin haske kan soke rundunar ‘yan sanda ta musamman mai yaki da ‘yan fashi da makami wato “Special Anti Robbery Squad” ko SARS a takaice, wacce yanzu ana tsara kafa wata sabuwar runduna da zata maye gurbinta.
A jiya Litinin ne aka fara sauraren bahasin tabbatar da Any Coney Barret wacce za a nada alkaliyar kotun kolin Amurka a Washington, inda Barrett ta fadawa majalisar dattawa cewa bakamata kotuna su shata tsari ba, kamata ya yi su bar wa shugabannin Amurka da majalisar dokoki.
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya WHO, jan hankali game da ikirarı da Kasashe da dama ke yi na cewa sun gano hanyoyi da magunguna na dakile cutar COVID -19 wanda ba wanda hukumar lafiya ta duniya ce a amince da su ba.
Yau litinin daliban makarantun firamare da na sakandare a jihar Kano ke komawa ajujuwa domin fara daukar darasi bayan shafe fiye da watanni bakwai a gida sandiyya annobar Corona.
A kalla malaman makaranta 3,000 a kasar Kamaru sun ki amincewa da tayin da rundunar sojin kasar ta yi musu na jigilarsu zuwa makarantunsu a yankin da masu amfani da harshen turanci da ake tashin hankali.
Jinkiri da mahukunta suke yi wurin nadin sabon sarkin Zazzau na ci gaba da jawo cece-kuce da kuma yada labarai mabanbanta game da masarautar, ciki har da maganar rarraba masarautar zuwa gida uku.
Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce ta kama wata mace mai suna Hauwa Habibu, mai shekaru 26 da haifuwa, wacce ke zaune a Diso Quarters a karamar hukumar Gwali ta jihar Kano bisa zargin kashe ‘yan’yanta biyu.
Shugaban kasar Ghana Nana Addo Dankwa Akufo-Addo ya gabatar da takardunsa na shiga takara a zaben shugaban kasa na ranar bakwai ga watan Disamba shekarar 2020 a kan tikitin jami’iyarsa ta New Patriotic Party ko NPP a takaice.
Yayin da ake haramar bude makarantu a Najeriya, hukumar dakile yaduwar cututtuka ta kasar NCDC, ta gana da masu ruwa da tsaki don sanin shirin da aka yi, yayin da a nata bangaren Kungiyar Malamai ke nuna damuwarta kan wannan batu.
Yau biyar ga watan Oktoba kasashen duniya ke bikin tunawa da ranar malaman makaranta wace Majalisar Dinkin Duniya ta ware domin karrama malamai saboda gudunmuwar da suke bayarwa wajen ilmantar da al’umomin duniya.
‘Yan Sanda a birnin Minsk na kasar Belarus sun yi amfani da tankar ruwan zafi wajen tarwatsa taron jama’a yayin da ake ci gaba da zanga-zangar kin jinin shugaba Alexander Lukashenko a Lahadi ta tara a jere. A kalla mutane dubu 100,000 suka fito kan tituna a birnin a jiya Lahadi.
Hukumar Hisbah a jihar Sokoto ta ce ta kammala bincike a kan hotunan tsiraici na wata yarinya da aka yada inda ake zargin wani dan babban jami'in gwamnatin jihar Sokoton, to amma kuma kwatsam sai gwamnati ta ba da sanarwar dakatar da ayyuukan hukumar.
Bayan wani hari da aka kaiwa tawagar Gwamnan jihar Borno Prof Baba Gana Umara Zulum a ranar jumma'a alumman jihar na ci gaba da bayyana ra'ayinsu a kan lamarin, da ma abin da ya shafi tsaro a jihar baki daya.
Bayan kusan shekaru hudu da dan takaran shugaban kasa a waccan lokaci Donald Trump ya fuskanci tambayoyi a kan biyan haraji yayin wata mahawara da aka yayata a telbijin kasa baki daya
batun zaben kasar Belarus na ci gaba da daukar hankalin kasashen duniya, bayanda kasar ta shiga rudani biyo bayan sanar da sakamakon zaben da Shugaban Kasar Belarus Alexander Lukashenko ya baiwa kansa nasara
Kungiyar Kwadagon Najeriya ta NLC da gamayyar kungiyoyin kwadago ta TUC, sun janye yajin aikin gama-gari da suka shirya shiga yau Litinin, 28 ga watan Satumban shekarar 2020, akan karin farashin man fetur da wutar lantarki.
Shugaban Amurka Donald Trump ya fada a jiya Lahadi cewa zai bukaci abokin takararsa na jam’iyar Demokrat a babban zaben uku ga watan Nuwamba, tsohon mataimakin shugaban kasa Joe Biden, da yayi gwajin kwayoyi kafin ko bayan muhawararsu ta ranar Talata.
Wuni guda bayan jana’izar Kanar Bako, babban hafsan sojojin Najeriya ya jinjinawa kwmandan soji Kanar DC Bako da Mayakan kungiyar Boko Haram suka kashe
Domin Kari