Yemi Mobolade, dan Najeriya ne kuma dan kasuwa wanda bashi da kwarewa a harkar siyasa, ya zama bakar fata na farko da aka taba zaba a matsayin Magajin Garin Colorado Springs bayan da yayi nasara akan Wayne Williams da daren Talata a zagayen zaben da aka yi a birnin.
Jami'i mai kula da al'amuran mu'amala da jamma'a Muntari Yusuf Ibrahim ne ya fitar da sanarwa cewa “an lura da yadda ake samun gajimare a wasu yankunan arewacin kasar kamar Borno, Taraba, Gombe, Bauchi da Kano, wanda ake sa ran zai kada yammaci ya haifar da yanayi makamancin na farko a wasu birane."
Prigozhin wanda ya kasance makusancin shugaban kasar Rasha Vladimir Putin, a fili, ya yi barazanar janye mayakansa daga yankin Bakhmut, inda suke kan gaba wajen farmakin da Rasha take kaiwa, har sai dai idan sun samu makaman da suke bukata.
Ta yiwu a je zagaye na biyu a zaben shugaban kasar Turkiyya da aka gudanar a jiya Lahadi bayan da Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan, wanda ya kwashe shekaru 20 yana mulkin kasar, ya kasa samun cikakkiyar nasara akan babban abokin karawarsa a zaben.
Tsaftattacen ruwan sha, lafiyar muhalli, da tsaftar jiki su na taka mahimmiyar rawa wajen samar da ingantacciyar lafiya da kuma kasancewa cikin koshin lafiya
La'akari Da yadda wasu al'adu ko dabi'un al'umma a wasu yankunan Najeriya suke kara kawo matsin a rayuwa musamman ga marasa karfi daga cikin al'umma, gwamnatin jihar Sokoto take kokarin haramta yin almubazzaranci a lokacin bukukuwa.
Rahoton da Ofishin kula da basussuka ya fitar na kwata na hudu na shekarar 2022 ya nuna cewa jimlar bashin da ake bin Najeriya a wannan lokacin ya haura Naira Triliyan 46.25
Yayin da Gwamna Akeredolu ya ki amincewa da tsarin da APC ta fitar na shugabancin majalisa ta 10, Betara ya ce babu gudu ba ja da baya game da takarar shi na neman shugabancin majalisar sannan gamayyar hadin kan ‘yan arewa a majalisar ta ki amincewa da zaben Apkabio da Abbas.
Tun gabanin gudanar da zabukan da suka gabata a Najeriya batagarin matasa ke barazana ga mazauna birnin Kano ta hanyar kwace musu wayoyin, musamman a wasu yankuna na birnin walau da rana ko da daddare.
Kusan jarirai miliyan daya ne suke mutuwa a kowace shekara, bisa dalilan da suka shafi yanayin haihuwarsu bakwanni, kana, an gano cewa babu wani saukin da aka samu game da lamarin a fadin duniya baki daya cikin shekaru goma da suke wuce daga shekara to 2010 zuwa 2020.
Kotu ta umurci Tsohon shugaban Amurka Donald ya biya matar da aka tabbatar ya yi ci zarafinta ta hanyar neman yin lalata da ita shekaru da dama da suka wuce, lamarin da Trump ya sha musantawa a baya.
Kusan makonni uku kenan tun bayan da wani rikici tsakanin manoma da makiyaya ya yi sanadin rasa rayuka da kone-konen gidaje, yayin da mutanen kauyukan da ke kewaye da garin na Tattara suka yi gudun hijira zuwa garin Garaku, shalkwatar karamar hukumar Kokona a jihar Nasarawa.
A cigaba da gwagwarmayar neman shugabancin Majalisar wakilan Najeriya na 10, mutane hudu da suke neman shugabancin sun hada kansu domin doke zabin masu fada a ji a jam'iyyar APC a Lagos kuma zabin zababben shugaban kasa Tajkudeen Abbass.
Allah ya kiyaye aukuwar wani hadarin jirgin sama mallakin Max air bayan da tayar jirgin ta fashe da ya ke yunkurin sauka a titin jiragen saman dake babbar tashar jiragen sama na Nnamdi Azikiwe dake Abuja.
Daruruwan ‘yan Najeriyan da suka guje wa rikicin Sudan sun sauka a filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe bayan an fuskanci tasgaro wajen jigilarsu zuwa kasar Masar inda suka kwashe kwanaki a cikin Hamada cikin matsanancin yanayin rashin ruwa da abinci da rashin tabbacin abin da ka iya biyo baya.
Cibiyar bincike da maganin cutar daji NICRAT ta bayyana damuwarta a game da rahoton samun sinadarin ethylene oxide a cikin INDOMIE INSTANT Noodles na musamman mai dandanon kaza.
Yan majalisar Najeriya masu jiran gado daga jam'iyya mai ci da na 'yan adawa sun hada kai wajen kafa wata kungiya mai suna JOINT TASK-10TH ASSEMBLY a turanci, wacce za ta tabbatar da goyon bayan duk wani shiri na shiya shiya da jamiyya mai mulki ta fitar domin zaben shugabanin majalisar.
Domin Kari