Kwamitin Majalisar Dattawan Najeriya da ta kafa a karkashin shugabancin Senata Aliyu Magatakardan Wamako domin ya binciki badakalar da ake zargin an tafka a kamfanin NNPC zai fara zamansa yau
WASHINGTON DC —
Shugaban kwamitin binciken, Senata Aliyu Magatakardan Wammako, a zantawar da yayi da wakilinmu Saleh Shehu Ashaka ya bayyana hakan.
Shugaban kwamitin yace, a zamansu na yau ne zasu tantance tsarin aikin da aka basu da kuma yadda zasu gudanar da shi.
Dangane da cewa ko an kafa kwamitin din ne domin a ci wa wasu zarafi, Senata Aliyu yace ba za’a yi anfani dasu ba a muzgunawa wani,zasu yi aikin ne tsakaninsu da Allah, ta yadda zasu taimakawa Shugaba Muhammad Buhari a yakin da yake yi da cin hanci da rashawa.
Ga rahoton Saleh Ashaka da karin bayani
Your browser doesn’t support HTML5
Yau Kwamitin da Zai Binciki Kamfanin NNPC Zai Yi Zaman Farko - 1' 47"