Shugaban wanda ya fara da jihar Jigawa a jadawalin kewaya jahohin Najeriya da ya tsara, domin ganawa da magoya baya gabanin taron kolin jam’iyyar ta PDP da za a yi a watan gobe, yace hakan na daga cikin alkawarinsa na farfado da ruhin jam’iyyar.
Shi kuma tsohon gwamnan jihar Jigawa Sule Lamido, dake zaman babban mai masaukin baki ya yi jawabi a taron inda ya furta kalaman da ke koda sabon shugaban Jam’iyyar Ali Modu, yayi kuma fatan sake karbar ikon jihar a zaben shekara ta 2019.
Dangane da tsarin yar tinke da PDP tace zatayi amfani da shi wajen fitar da yan takara a zaben 2019, Ambasada Kazaure yace, yin hakan zai nunawa Najeriya cewa Dimokaradiyya ta nuna a wajen yan PDP, haka kuma za a gudanar da hakan ba tare da samun tangarda ba, harma da zaben wanda jama’a ke so.
Saurari rahotan don karin bayani.
Your browser doesn’t support HTML5
PDP Na Daukar Matakan Kwace Madafun Iko A Najeriya - 2'57"