Ministan harkokin wajen Korea ta Arewa yace Amurka ta ayyana yaki da kasarsa

Shugabannin Korea ta Arewa

Ministan harkokin wajen Korea ta Arewa Ri Yong Ho yace Amurka ta ayyana yaki da kasarsa kuma kasar sa zata mayar da martini, ciki har da harbo jiragen saman yakin Amurka dake yankin, idan ta ci gaba da yi mata barazana.

Kai tsaye Ri ya danganta kalaman shugaban na Amurka Donald Trump a ranar Asabar da ya dora a shafin sada zumunta da wannan barazana. Da yake maida martani a kan jawabin Ri a wurin babban taron MDD tun da farko, Trump ya rubuta cewar, yanzu y agama sauraren ministan harkokin Korea ta Arewa a MDD. Idan ya maimaita kalaman mutumin nan mai kananan rokoki, zai yi kaca kaca dasu.

A yau Litinin ministan harkokin wajen Korea ta Arewa ya maida martani a kan wannan batu.

Yace ganin wadannan kalaman sun fito daga bakin wanda ke shugabancin Amurka, ko shakka babu yaki ne aka ayyana, inji Ri yana fadawa manema labarai a otal din da yake zaune a birnin New York. Yace kasashen da suke halartan taron MDD da ma duniya baki daya su tuna da cewar Amurka ce ta fara kada gangar yaki a kan kasarsa.

Ministan na Korea ta Arewa ya kara da cewar, zasu samu hurumin daukar matakan mayar da martani, ciki har da harbe jiragen yakin Amurka koda kuwa basu karaso a sararin samaniyar kasarsa ba a wani kashedi da yayi.