Kaucewa Rashin Sakin 'Yan Wasa Da Wuri In Ji NFF

Hukumar kwallon kafar Najeriya ta NFF, ta ba da tabbacin cewa za ta gana da kungiyoyin kwallon kafa na Premier League a Najeriya, domin a tabbatar an saki ‘yan wasa akan kari kafin karawar da Super Eagles za ta yi da ‘yan wasan Rwanda a wasan neman gurbin shiga gasar cin kofin Nahiyar Afrika da za a yi a shekara mai zuwa.

Hakan na faruwa ne a daidai lokacin da kocin ‘yan wasan Najeriya na ‘yan kasa da shekaru 23, Samson Siasia, ya ke kokarin shima ya hada kan ‘yan wasan da za su kara a wasan neman gurbin shiga gasar cin kofin nahiyar afrika ta ‘yan kasa da shekaru 23 a Senegal.

Hukumar ta NFF, na kokari ta hadu da kungiyoyin ne domin a kaucewa aukuwar abinda ya faru a baya kafin gasar da za a yi a farkon shekara mai zuwa a cewar wata majiya da ta gana shafin wasanni nan a yanar gizo da ake kira Completesportsnigeria.com.

Zai dai a buga gasar ta cin kofin nahiyar Afrika ne a tsakanin 16 ga watan Jainairu zuwa 6 ga watan Fabrairun shekara mai zuwa a biranen Kigali da Gisenyi da Bature da ke kasar Rwanda.

Ana sa ran kakar wasan gasar Premier ta Najeriya za ta kare ne a wannan wata na Nuwamba inda za a dawo a watan Janairu domin fara wata sabuwar kakar wasa.