Shugaban kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan a ranar Laraba ya kai ziyararsa ta farko a Masar tun shekara ta 2012, inda ya gana da Shugaba Abdel Fattah al-Sisi
WASHINGTON, D. C. - Wanda hakan wani babban mataki ne da shugaban na Türkiye ya dauka na sake gina alaka tsakanin kasashen yankin.
Egypt/Turkey
Erdogan ya ce tattaunawar ta su za ta mayar da hankali ne kan hare-haren da Isra'ila ke kaiwa zirin Gaza.
Egypt/Turkey
Shugabannin da dangantakarsu ta yi tsami tun juyin mulkin da sojoji suka yi a Masar a shekara ta 2013 da kuma watsewar kungiyar 'yan uwa musulmi wato Muslim Brotherhood, za su gudanar da wani taron manema labarai bayan sun gama tattaunawa.