Anya Kuwa Zaben Kananan Hukumomi Zai Yiwu a Borno Tsakanin Watan Afrilu da Yuli?
Gwamnan Jihar Borno, Kashim Shettima.
Ra'ayoyin manyan shugbannin siyasar jahar Borno sun bambanta game da yin zaben kananan hukumomi
WASHINGTON, DC —
Gwamnan jahar Borno Kashim Shettima ya bayyana aniyar gudanar da zabe a kananan hukumomin jahar ishirin da bakwai tsakanin watan afrilu da yuli mai zuwa.
Your browser doesn’t support HTML5
Zaben kananan hukumomi zai yiwu a Borno kuwa? - 2:24
An dade ba a yi zaben kananan hukumomi a jahar ta Borno ba saboda rigingimu da tashe-tashen hankulan da su ka sa shugaban kasa Goodluck Jonathan ya kafa dokar ta baci a jahar ta Borno da makwaftan ta biyu wato Adamawa da Yobe.
Wakilin Sashen Hausa a jahar Borno Haruna Dauda Biu ne ya aiko da wannan rahoto.