A yau Litinin aka rantsar da Bola Tinubu a matsayin shugaban kasar Najeriya, bayan da aka gudanar da zaben cike gurbi da kuma fuskantar matsin lamba kan ya gaggauta inganta yanayin tattalin arziki da tsaro.
washington dc —
Lamarin da wasu da dama ke korafin ya kara tabarbarewa a zamanin tsohon shugaban kasar Muhammadu Buhari.
An rantsar da Tinubu ne a wani biki da aka yi a dandalin Eagle Square da ke babban birnin tarayya Abuja, wanda ya samu halartar manyan baki na ciki da wajen kasar.
Your browser doesn’t support HTML5
An Rantsar Da Bola Tinubu A Matsayin Shugaban Kasar Najeriya
Biyu daga cikin manyan abokan hamayyar Tinubu a zaben watan Fabrairu na kalubalantar nasarar da ya samu a kan zargin magudi. A ranar Talata ne za a fara zaman kotun domin sauraren manyan hukunce-hukuncensu, inda ba a sa ran yanke hukuncin ba kafin watan Satumba.