Rashin kundin dai na da nasaba da sauyin launin kudi da aka yi a Najeriya, lamarin da ya sa har yanzu hada-hadar kudi ta kasa daidaita a kasar kuma a daidai lokacin da aka fara azumin watan Ramadan.
Wannan dai ya zamo wani babban kalubale musamman idan aka yi la’akari da cewa mafi yawan masu kayayyakin da aka fi bukata a cikin watan Ramadan basa tu’ammali da na’urar zamani ta hada-hadar kudi.
A babbar kasuwar Wuse da ke babban birnin tarayya Abuja, wasu ‘yan kasuwa sun ce farashin kayayyaki na hauhawa, don ko a wannan satin shinkafar tuwo da aka saida naira dubu talatin da hudu ta kai dubu talatin da bakwai.
GOMBE: Farashin shinkafa da sauran hatsi ya sauka
A lokacin azumi dai akan bukaci kayan marmari kamar lemu, mangwaro, kankana, ayaba da sauransu.
Zaharaddin Nuhu, dan kasuwa ne mai saida kayan marmari, ya ce babu abinda ya canza a farashin kayan marmari kuma yana fatan ba za a samu kari ba a farashin.
Wasu ‘yan kasuwa dai sun bayyana tsarin hada-hadar kasuwanci ba tare da musayar tsabar kudi ba a matsayin wani babban ci gaba, yayin da wasu ke ganin hakan na kawo tarnaki ga tsarin kasuwanci.
VENEZUELA-CREDIT/
Sai dai mafi akasari ‘yan kasuwar da ke karkara na kokawa kan sabon tsarin na kasuwanci ba tare da musayar tsabar kudi ba.
Saurari rahoton Hauwa Umar:
Your browser doesn’t support HTML5
‘Yan Kasuwa Sun Koka Kan Rashin Kudi Yayin Da Ake Gab Da Fara Azumi