Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Zancen Tattaunawa Kan Saukar Gaddafi Ba Ta Taso Ba a Cewar Firayim Minista


Dakarun 'yan tawayen Indiya
Dakarun 'yan tawayen Indiya

Firayim Ministan Libya yace sam, ba wata tattaunawa da zasuyi da kowa a duniya gameda wai

Firayim Ministan Libya yace sam, ba wata tattaunawa da zasuyi da kowa a duniya gameda wai ko shugaban Libya Muammar Ghadafi ya zauna a kasar ko ya barta, yaje wani gun.

Haka kuma Farayim Minista din, Al-Ba ghdadi al-Mahmoudi ya fada a yau cewa ba wata tataunawar arziki da zasuyi da kowa akan rikicin siyasar kasar muddin ba a ja burki ga abinda ya kira “gallazawar NATO” ba.

Firayim Ministan yana wannan kalamin ne jim kadan bayan ganawarsa da wani manzon musamman na Majalisar Dinkin Duniya (Abdul Elah al-Kahtib) wanda shi kuma jiya-jiya ya gama saduwa da jagabannin ‘yantawayen Libya din.

sai dai, da take maida murtani ga wadanan kalaman a birnin Brussels. wata mai magana da yawun NATO tace za’a ci gaba da fatattakar da sojan NATO ke yiwa Libya har zuwa lokacinda bukatar yin hakan ta kau.

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 2:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG