Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

‘Yan Tawayen Houthis Sun Sha Alwashin Ci Gaba Da Kai Hare-Hare Don Nuna Goyon Bayan Falasdinawa


‘Yan Tawayen Houthis
‘Yan Tawayen Houthis

Houthis na kasar Yemen da ke samun goyon bayan Iran, za su ci gaba da kai hare-hare kan jiragen ruwa na tekun Bahar Rum domin nuna goyon bayansu ga Falasdinawa muddin Isra'ila ta ci gaba da aikata laifuka a kansu, in ji shugabansu a ranar Alhamis.

Abdulmalik al-Houthi ya fada a wani jawabi da ya yi ta gidan telebijin cewa "Ayyukanmu na da matukar tasiri ga makiya kuma mun samu babban nasara."

Ya ce kungiyar za ta ci gaba da tallafa wa Falasdinawa duk da hare-haren da Amurka da Burtaniya ke kai wa kan mayakan Houthin a Yemen a matsayin ramuwar gayya kan hare-haren da Houthi ke kaiwa kan jiragen ruwa na kasa da kasa a tekun Bahar Rum.

Hare-haren na Bahar Rum dai sun kawo cikas ga jigilar kayayyaki a duniya tare da tilasta wa kamfanoni sake hanya mai tsawo da kuma tsada a kudancin Afirka, kuma ya haifar da fargaban cewa yakin Isra'ila da Hamas na iya yaduwa tare da hargitsa Gabas ta Tsakiya.

~ REUTERS

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 3:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 2:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG