Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Taliban Ta Tabbatar Da Kashe 'Ya'yanta 21


'Yan Taliban
'Yan Taliban

Kungiyar nan da doka ta haramtata a Pakistan ta Taliban, tabbatar da kashe mambobinta 21 a samame da wani jirgin Amurka mara matuki ya kai a makwabciya Afghanistan a ranar Laraba da ta gabata.

Harin da aka kai a gudnumar Kunar dake kan iyakar gabashin Afghanistan, ya auna sansanin horar da mayakan kungiyar nan da take kiran kanta Terik-e-Taliban ko kuma TTP a takaice, inda ake horar da masu kunar bakin wake, a cewar jami’an leken asirin Afghanistan da na Pakistan.

Jami’an sun ce galibin kwamandojin mayakan da kuma kwararrun masu bada horo a sansanin, suna cikin mutanen da aka kashe, wadanda suke shirin kaddamar da kai hare haren kunar bakin wake a Pakistan.

Kungiyar ta TTP ta fitar da wata sanarwa a jiay Juma’a, kuma ta tabbatar da kashe wani matashi dan kasa da shekaru 20, dan shugaban kungiyar, Mullah Fazullah kuma kungiyar ta sha alwashin daukar fansa a kan mummunar farmakin. Kungiyar 'yan ta’addan tace harin da jirgin Amurka mara matukin ya kai, ya taba makarantar addini kuma ya kashe daliban makaratantar da malamansu.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG