Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Najeriya Na Dab Da Tilastawa Ma’aikatun Gwamnati Ware Kaso 5 Cikin 100 Na Guraben Aikin Yi Ga Masu Bukata Ta Musamman


Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu
Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu

Gwamnatin Tarayya na dab da fara aiwatar da shirinta na tillastawa hukumomi da ma’aikatun gwamnati ware kaso 5 cikin 100 na guraben aikin yi ga masu bukata ta musamman a fadin Najeriya.

Gwamnatin Tarayya na dab da fara aiwatar da shirinta na tillastawa hukumomi da ma’aikatun gwamnati ware kaso 5 cikin 100 na guraben aikin yi ga masu bukata ta musamman a fadin Najeriya.

Babban Hadimin Shugaban Kasa Bola Tinubu akan Masu Bukata Ta Musamman, Muhammad Abba-Isa ne ya bayyana hakan a birnin Damaturu, fadar gwamnatin jihar Yobe, a yayin wata ganawa da masu bukata ta musamman da sauran masu ruwa da tsaki bayan bashi mukamin.

Ya bayyana cewar offishinsa na aiki kafada da kafada da Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya domin tallafawa masu buakata ta musamman, da nufin rage su akan tituna suna barace-barace.

“Wajibi ne hukumomi da ma’aikatun gwamnati su warewa masu bukata ta musamman kaso 5 cikin 100 na guraben aikin yi, domin hanya daya tilo ta rage musu radadin rayuwa ita ce ta samu musu ayyukan yi da tallafi.

“Kuma ita ce kadai hanyar magance yawan barace-barace kuma nan gaba kadan Shugaban Kasa zai bayyana shirye-shirye da tsare-tsare akan hakan”.

“An riga an fitar da sanarwa daga ofishin sakataren gwamnatin tarayya da nawa ofishin domin yin matsin lamba ga hukumomin. Muna da shiri a kasa, abinda ke mana cikas kawai shine, yadda za’a aiwatar da shirin.” a cewar Abba Isa.

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 3:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 2:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG