Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Jami'iyar Adawa ta Nan Amurka ta Maida Martani a Kan Jawabin Shugaba Trump


Dan majalisar wakilai na Jami'iyar Democrat, Joe Kennedy na uku, Yana Maida Martani ga Shugaba Trump
Dan majalisar wakilai na Jami'iyar Democrat, Joe Kennedy na uku, Yana Maida Martani ga Shugaba Trump

Dan majalisar wakilai Joe Kennedy na uku na jami’iyar Democrat mai wakiltan Massachusetts ya maida martani a kan jawabin shugaba Donald Trump yayi ga kasa.

Yace muna a nan birnin Fall River a jihar Massachusetts, birni da Amurka ke alfahari da ita wanda bakin haure suka ginata.


Yace munga tattalin arziki da saka jari yayi tashin goron zabi, amfani masu zuba jari yayi kauri, kampanoni suka samu kazamin riba amma kuma suka gaza raba amfani ga ma’aikata.


Mun ga gwamnati da tayi ta fifitukar ganin ta ci gaba da gudanar da aiyukanta.


Kasar Rasha kuma ta zo tayi dumu dumu ta shiga ko kuma ta yi katsalanda a demokaradiyarmu


Yace ana yaki a kan kare muhalli.

Ya ci gaba da cewa, za a iya yin shewa ga alkauran da yan siyasa suka dauka, amma kuma za a yanke wa kasa hukunci ne a kan alkauran da ta cikawa jama’arta.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG