Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Gwamnati da 'Yan Tawayen Sudan Ta Kudu Su Koma Teburin Shawara - Amurka


Shugaban Sudan Ta Kudu Salva Kiir
Shugaban Sudan Ta Kudu Salva Kiir

Kasar Amurka da ta taimaka aka samu Sudan Ta Kudu tace alatilas bangarorin biyu dake fafatawa da juna su koma teburin shawara

Tawagar kasar Amurka zuwa kasar Sudan ta Kudu ta bukaci bangarorin biyu masu fada da juna da su sake darewa kan teburin sulhu.

Wannan shawara dai tazo ne kwana daya bayan da Majalisar Dinkin Duniya tayi gargadincewa duk wanda ke kawo wa tsarin zaman lafiya barazana to zata kakaba masa takunkunmi.

Jakada Donald Booth ya fada wa taron manema labarai a babban birnin kasarna Juba cewa hanyar samar da zaman lafiya da lumana shine ta tattaunawa tsakanin bangarorin biyu.

Booth ya jaddada cewa kudirin kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya shine tankunkumin ba zai kyale wasu daidaikun mutane ba na kasar masu kawo wazaman lafiya cikas.

Yace duka bangarorin suna anfani da dodorido domin shuka tsoro a zukatan wasu yan kasan

Ita dai kasar Sudan Ta Kudu ta samu damar zamowa kasa ce mai yancin cin gashin kanta daga tsohuwar kasar Sudan ta arewa a shekarar 2011 tare da goyon bayan Amurka.

Amma kwaran kuma sai yaki ya barke tsakanin su a cikin watan disembar shekarar 2013 bayan da shugaban kasar Salva Kirr ya zargi mataimakinsa Riek Machar da kokarin yi masa juyin mulki.

Yanzu haka dai fada a wannan kasar ta Arewacin Africa yayi musabbabin kashe dubban mutane kana ya raba sama da miliyan 2 da muhallansu. Yanzu kasashen duniya suna ta kokarin ganin an samu zaman lafiya a wannan kasar amma shugaba Salva Kirr da mataimakin nasa Marchar sun kasa su cimma matsaya akan rabon iko idan an zo kafa gwwamnatin hadin kan kasa

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG