Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Dalilin Da Ya Sa Muka Rufe Asusun Ma’aikatun Gwamnati - Gwamnan Kano


Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf (Hoto: Facebook/Abba Kabir Yusuf)
Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf (Hoto: Facebook/Abba Kabir Yusuf)

Gwamna Kabir ya yi kira ga masu biyan haraji da su kwantar da hankalinsu yana mai ba su tabbacin cewa za a yi amfani da kudaden ta hanyoyin da suka kamata.

Gwamnan jihar Kano da ke arewa maso yammacin Najeriya Abba Kabir Yusuf, ya ba da umarnin rufe daukacin asusun ma’aikatun jihar a ranar Laraba.

Yusuf ya ba da umarnin ne yayin wani taro da ya hada da shugaban hukumar harajin jihar da shugabannin ma’aikatun gwamnati a cewar rahotanni.

An ba akanta-janar na jihar umarnin da ya rufe daukacin asusun adana kudaden ma’aikatun a wani mataki na tabbatar da ana kashe su ta hanyar da ta dace.

Ana kuma sa ran bankuna za su mika takardun shaidar bin wannan umarni daga fadar gwamnatin don a tabbatar an rufe asusun.

Gwamna Kabir ya yi kira ga masu biyan haraji da su kwantar da hankalinsu yana mai ba su tabbacin cewa za a yi amfani da kudaden ta hanyoyin da suka kamata.

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 3:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG