Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Bincike ya Nuna Gurbataccen Iska Yafi Kashe Mutane a Duniya


People wearing face masks walk past cars clogged with heavy traffic on a road as Beijing is hit by polluted air and sandstorm, May 4, 2017. Authorities in Beijing issued a blue alert on air pollution as sandstorm swept through the Chinese capital city on
People wearing face masks walk past cars clogged with heavy traffic on a road as Beijing is hit by polluted air and sandstorm, May 4, 2017. Authorities in Beijing issued a blue alert on air pollution as sandstorm swept through the Chinese capital city on

Wani sabon bincike yace abubuwa da suka fi kashe mutane kuma suke haddasa mutuwa farab daya sune yaki, ta’addanci, bala'oi daga Allah, da tabar sigari da kuma cututtuka.

Bincike da aka wallafa a mujallar labaran kiwon lafiya ta Lancet yace, gurbataccen iska wanda ke fili da na cikin wani abu, sun kashe mutane miliyon tara a shekarar 2015, ko kuma sune sanadin daya a cikin kowace mutuwa shida.

A India iska mai guba dake tashi daga kone-kone wasu sanadari tana shiga babban birnin kasar inda miliyoyin mutane ke zaune. Birnin New Delhi ne kan gaba a fadin duniya inda mututne suka fi mutuwa sakamakon gurbatar yanayi.

Wanda ya wallafa bincike yace gurbatar iska na barazana ga yancin bil adama, kamar yancin rayuwa, yancin samun koshin lafiya, yancin kyautatuwar rayuwa da kuma yancin kare yara da marasa galihu.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG